in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jagoran 'yan adawa na kasar Kenya ya yi zargin an yiwa tsarin tattara zaben kasar kutse
2017-08-09 19:27:06 cri
Jagoran 'yan adawa na kasar Kenya Raila Odinga ya yi fatali da sakamakon zaben kasar na ranar Talata, wanda ke nuna cewa, shugaban kasar mai ci Uhuru Kenyatta ne ke kan gaba. Yana mai zargin cewa, wasu sun yiwa na'urorin tattara sakamakon zabe na hukumar zaben kasar kutse, inda suka canja alkaluman zaben.

Sakamakon farko na zaben, ya nuna cewa, shugaba Uhuru Kenyatta ya samu kuri'u miliyan 7.77 kimanin kaso 54 cikin 100, yayin da abokin takararsa Raila Odinga ya samu kuri'u miliyan 6.39, kimanin kaso 44 cikin 100 na yawan kuri'un da aka kada.

A cewar jagoran adawar, wasu masu kutse da ba a san ko su wane ne ba, sun yiwa na'urar tattara sakamakon hukumar zaben kasar kutse, domin hana shi lashe zaben shugabancin kasar na jiya Talata. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China