in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana maraba da sassauta yanayin tashin hankali a Jerusalem, in ji babban magatakardan MDD
2017-07-28 13:46:05 cri
A jiya Alhamis ne babban magatakardan MDD Antoni Guterres, ya fidda wata sanarwa dake yabawa kyautatuwar al'amura, bayan tashin hankali a tsohon birnin Kudus.

Mr. Guterres ya ce, ana fatan bangarorin da abin ya shafa za su ci gaba da shawarwari tsakaninsu domin karfafa fahimtar juna. Kaza lika zai ci gaba da yin cudanya da bangarorin da abin ya shafa.

A ranar 14 ga watan nan da muke ciki ne, 'yan sandan Isra'ila guda biyu sun rasu sakamakon harin da aka kai musu a masallacin Kudus, bayan hakan ne kuma Isra'ila ta sa wata kofar binciken jikin masu shiga masallacin, lamarin da ya haddasa dauki ba dadi tsakanin Isra'ila da tsagin Falesdinawa, kuma ya zuwa yanzu, hakan ya haddasa rasuwar mutane 10, yayin da wasu kimanin 500 suka jikkata.

A ranar 25 ga wata, hukumar tsaron Isra'ila ta tsai da kudurin kau da wannan kofa ta bincike. Har wa yau a ranar 27 ga wata, limamin al'ummar musulmi a birnin na kudus Sheikh Muhamad Ahmad Hussein, ya sanar da kawo karshen tashin hankali tsakanin Isra'ila da Palasdinawa kan wannan batu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China