in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan Afrika masu neman mafaka a Israel sun yi maci don nuna adawa da dokar rage musu albashi
2017-06-11 12:28:26 cri
Daruruwan 'yan Afrika dake neman mafaka sun yi zanga zanga a titunan birnin Tel Aviv na kasar Isra'ila, inda suke nuna adawa da sabuwar dokar zaftare kashi 20 cikin 100 na albashinsu.

Karkashin sabuwar dokar, wadda ta fara aiki tun a ranar 1 ga watan Mayu, dokar ta nemi ma'aikatan su ajiye kashi 20 cikin 100 na kudaden da suke samu a wani asusu na kasar. Kuma zasu iya samun kudaden da suka ajiye ne a lokacin da bakin masu neman mafakar zasu bar kasar Isra'ilan.

Ma'aikata 'yan cin ranin sun gudanar da zanga zangar ne tare da wasu 'yan asalin kasar Isra'ilan dake musu goyon baya, daga cikinsu akwai masu gidajen abinci, wadanda su ne mafi yawan ma'aikatan 'yan ciranin dake Tel Aviv ke musu aiki.

Wata kididdiga da mahukuntan kasar suka bayar ta nuna cewa, ya zuwa karshen watan Fabrairu, kimanin baki dubu 22 ne ke neman mafaka a Israilan. Kuma mafi yawansu sun zo ne daga kasashen Eritrea da Sudan.

Karkashin dokokin Israeli da na kasa da kasa, basu amince a tusa keyar masu neman mafakar zuwa kasashensu na ainihi ba, indan zasu iya fuskantar hukuncin kisa.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China