Mahukuntan jihar Xinjiang mai cin gashin kanta dake arewa maso yammacin kasar Sin, sun bayyana shirin fara jigilar fasinjoji ta jiragen sama tsakanin gundumar Shache zuwa birnin Urumqi, hedkwatar jihar, tun daga ranar 1 ga watan Agusta mai zuwa.
An dai fara ginin filin sauka da tashin jiragen sama da zai hada sassan jihar biyu ne tun a shekarar 2015. Ana kuma fatan bayan fara sufuri, fasinjojin da za su yi zirga-zirga ta hanyar nan da shekarar 2020, za su kai mutum 200,000.