in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu gagarumin ci gaba game da kare hakkin bil-Adam a yankin Xinjiang
2017-06-01 15:26:46 cri
Wata farar takarda da majalisar gudanar kasar Sin ta fitar a jiya Alhamis ta yaba matuka game da gagarumin ci gaban da aka samu a fannin kare hakkin al'ummomin kungiyoyin kabilu daban-daban dake yankin Xinjiang na kabilar Uygur mai cin gashin kansa dake arewa maso yammacin kasar Sin.

A cewar takardar, mai taken "Hakkin bil-Adam a yankin Xinjiang--ci gaba da kuma nasarorin da aka cimma", tattalin arziki da jin dadin rayuwar al'ummar yankin ya shiga wani sabin babi a tarihi, tun lokacin da kasar Sin ta aiwatar da shirinta na bude kofa da zurfafa gyare-gyare a shekarar 1978.

Takardar ta kuma bayyana cewa, kafin kafa Jamhuriyar Jama'ar kasar Sin a shekarar 1949, kungiyoyin kabilu a yankin su ne kurar baya a fannin jin dadin rayuwa da batun kare hakkin bin-Adam.

Sai dai a 'yan shekarun nan, gwamnatin tsakiyar kasar Sin ta dauki matakan da suka dace na bunkasa tattalin arziki da rayuwar mazauna yankin. Matakin da ya taimaka wajen bunkasa ci gaba da kuma hadin kan kabilu, da kare muhimman hakkin bil-Adam na dukkan kungiyoyin kabilun dake yankin.

Takadar ta nanata kudurin mahukuntan kasar Sin na ci gaba da raya yankin da al'ummominsa, yayin da kwamitin tsakiya na JKS a nasa bangare ya taka muhimmiyar rawa wajen raya yankin. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China