Kwamitin tsaron MDD ya yi kakkausan suka game da harin da aka kaiwa dakarun wanzar da zaman lafiya a jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, lamarin da ya haddasa rasuwar jami'in tawagar dan kasar Morocco daya, tare da jikkatar wasu jami'an 3.
Cikin wata sanarwa da mambobin kwamitin su 15 suka fitar, sun soki harin na safiyar jiya Litinin, suna mai cewa hakan na iya zama laifin yaki bisa dokokin kasa da kasa.
Kwamitin na tsaro ya kuma bukaci mahukuntan jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da su gaggauta gudanar da bincike, tare da tabbatar da gurfanar da masu hannu cikin sa gaban shari'a. (Saminu)