in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya yi Allah wadai da kai hari ga mai kiyaye zaman lafiya a CAR
2016-06-29 14:00:20 cri
Kwamitin sulhun MDD ya bayar da wata sanarwa a jiya Talata, inda ya yi Allah wadai da kai hari ga wani mai kiyaye zaman lafiya na MDD a kasar Afirka ta Tsakiya CAR.

Sanarwar ta bayyana cewa, kasashe mambobin kwamitin sulhun sun yi Allah wadai da dukkan hare-haren da aka kai wa tawagar kiyaye zaman lafiya ta MDD dake kasar Afirka ta Tsakiya, duk wane irin harin da aka kaiwa masu kiyaye zaman lafiyar ya zama laifin aikata yaki.

Kwamitin sulhun ya yi kira ga gwamnatin kasar Afirka ta Tsakiya da ta yi bincike kan wannan hari cikin hanzari, ta kuma gurfanar wadanda ke da hannu a kai harin a gaban kotu. Mambobin kwamitin sulhun sun jaddada cewa, sun nuna goyon baya ga tawagar kiyaye zaman lafiya ta MDD dake kasar Afirka ta Tsakiya da ta taimakawa kasar wajen sake shimfida zaman lafiya a kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China