in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani sojon kiyaye tsaro na MDD ya rasu a Afirka ta Tsakiya
2017-01-07 13:32:28 cri
Kakakin babban magatakardan MDD Stephan Dujarric, ya bayyana a jiya cewa, an sake kai hari kan tawagar masu tabbatar da tsaro da MDD ta tura kasar Afirka ta Tsakiya, inda ya yi sanadin mutuwar wani soja dan kasar Bangladesh.

Mr. Dujarric ya ce, babban magatakardan MDD Antonio Guterres ya mika sakon ta'aziyya ga al'ummomi da gwamnatin kasar Bangladesh.

A 'yan shekarun nan, ana ci gaba da samun tashe-tashen hankula a kasar Afirka ta Tsakiya, musamman ma hare-haren da ake tsakanin dakaru masu dauke da makamai na kungiyar Anti Balaka da tsoffin mambobin kungiyar Seleka, lamarin da ya haddasa dimbin fararen hula su zama 'yan gudun hijira.

A halin yanzu kuma, ana ci gaba da fama da tashe-tashen hankula a kasar, ciki har da rikice-rikicen da ake tsakanin kabilu daban- daban, da kuma hare-haren da ake kai wa sojoji masu kiyaye tsaron kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China