in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi Allah wadai da kaiwa wani sojan kiyaye zaman lafiya na MDD hari a Afirka ta Tsakiya
2016-04-19 13:49:47 cri
A jiya Litinin ne kakakin babban sakataren MDD, Stephane Dujarric, ya bayyana cewa, an hallaka wani sojan kiyaye zaman lafiya na MDD, sakamakon harin da aka masa ranar Lahadi a Afirka ta Tsakiya. Ya ce Mr. Ban Ki-moon ya yi tir da aukuwar wannan danyen aiki.

Game da hakan Mr. Dujarric ya bayyana cewa bisa rahotannin da aka samu, dakarun kungiyar Lord's Resistance Army (LRA) ne suka kaddamar da harin a wani kauye dake kusa da garin Rafaï, na lardin Mbomou dake Afirka ta Tsakiya, sai dai daga bisani an tura wata rundunar soja ta MDD dake kasar zuwa wannan kauye.

Stephane Dujarric ya kara da cewa, Ban Ki-moon ya jaddada cewa, ba za a kyale duk wani mataki na kaiwa ma'aikatan kiyaye zaman lafiya, dake sadaukar da kansu domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar Afirka ta Tsakiya ba. Ya kuma yi kira ga gwamnatin kasar da ta dage wajen bankado tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan ta'asa gaban kotu.

A wani ci gaban kuma, a jiya Litinin ne kwamitin sulhun MDD ya fidda wata sanarwar dake Allah wadai kan wannan danyen aiki, inda sanarwar ta bayyana cewa, mai yiwuwa ne irin wannan harin da aka kaddamar ya zama laifin yaki. Sanarwar ta kuma kalubalanci gwamnatin Afirka ta Tsakiya da ta cafke masu hannu cikin wannan ta'asa. (Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China