in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a gaggauta shawarwari kan batun Syria, in ji wakilin Sin
2017-07-25 10:51:11 cri
Wakilin musamman na kasar Sin dake kula da batun kasar Syria Xie Xiaoyan ya bayyana a ranar 24 ga wata cewa, a halin yanzu, ana samun sauyin yanayin siyasa a kasar Syria, don haka ya kamata bangarorin da batun Syria ya shafa su yi amfani da damammaki masu kyau wajen ciyar da shawarwari a tsakaninsu gaba, ta yadda za a cimma ra'ayi daya kan wasu batutuwa masu alaka, domin warware matsalar kasar Syria yadda ya kamata.

Bugu da kari, jiya Litinin, Xie Xiaoyan ya jaddada a yayin taron manema labarai da aka yi a birnin Ankara na kasar Turkiyya cewa, kasar Sin za ta ci gaba da dukufa wajen inganta shawarwarin neman sulhu a tsakanin bangarorin da batun Syria ya shafa, domin neman ci gaba a fannoni guda hudu da suka hada da: tsagaita bude wuta, da gudanar da shawarwarin siyasa, da ba da taimakon jin kai, da kuma yaki da ta'addanci cikin hadin gwiwa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China