in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kwato filin da fadinsa ya wuce muraba'in kilomita 42000 daga hannun IS a kasar Syria
2017-07-16 12:52:04 cri
A cewar wata kungiyar kasa da kasa mai sa ido kan yanayin da kasar Syria ke ciki, dakarun SDF na kasar Syria da ke samun goyon baya daga kasar Amurka, sun samu nasarar kwato filayen kasar da fadinsu ya wuce muraba'in kilomita 42000 daga hannun kungiyar masu tsattsauran ra'ayi ta IS a kasar ta Syria.

Kungiyar SDF din mai kunshe da dakarun Kurdawa da Larabawa da sauransu tana kokarin kare yankunan dake karkashin kulawarta a wasu wuraren dake arewacin kasar Syria, bisa ga fadan da take yi da kungiyar IS. Kuma wata sabuwar nasarar da dakarun SDF suka samu ita ce, yadda suka samu nasarar mallakar karin ungwanni birnin Raqqa, wani garin dake arewacin kasar Syria, wanda ya kasance wata muhimmiyar mafaka ga kungiyar IS. Sai dai masu sa ido kan aikace-aikacen keta hakkin dan Adam a Syria sun ce, ko da yake dakarun SDF sun samu ci gaba a cikin birnin, amma har yanzu yake-yaken da suke yi tare da kungiyar IS ba su shiga cikin tsakiyar birnin ba tukuna.

Kungiyar SDF ta sanar da fara neman 'yantar da lardin Raqqa ne tun a ranar 6 ga watan Nuwamban shekarar 2016. Zuwa watan Yunin bana, ta fara samun babban ci gaban a yakin da take yi da dakarun na IS.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China