in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Lardin Hebei na kasar Sin zai kafa masana'antu a Najeriya
2017-07-20 15:46:34 cri

Wani jami'i a lardin Hebei na kasar Sin ya ce a shirye lardinsa yake wajen yin muhimmiyar hadin gwiwa da jahar Kaduna dake arewacin Najeriya.

Wang Xiaodong, mataimakin gwamnan lardin Hebei dake arewacin kasar Sin, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ziyara a jahar Kaduna, domin rattaba hannu kan yarjejeniyoyi da gwamnan Kadunan Nasiru El-Rufai.

Makasudin yin hadin gwiwa a tsakanin Hebei da Kaduna shi ne, domin kulla kyakkyawar dangantaka a tsakanin bangarorin 2 da kuma kafa masana'antu a jahar ta Kaduna.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China