in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
(Sabunta)Harin kunar bakin wake ya hallaka a kalla mutane 12 a Maiduguri
2017-07-17 20:33:26 cri
A kalla mutane 12 ne suka hallaka, sakamakon aukuwar wasu tagwayen hare haren kunar bakin wake a birnin Maiduguri fadar mulkin jihar Borno, dake arewa maso gabashin Najeriya.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, 'yan kunar bakin waken mata sun tada ababen fashewa a wani masallaci dake unguwar "London Chinki", lamarin da nan take ya sabbaba kisan mutane 10.

Daga bisani kuma aka ji tashin wasu ababen fashewar a Molai dake wajen birnin Maiduguri, wanda ya yi sanadiyar mutuwar a kalla wasu mutanen biyu.

To sai dai hukumar ba da agajin gaggawa ta Najeriyar ta ce mutane 8 ne aka tabbatar da rasuwar su, yayin da wasu karin mutanen 15 suka jikkata a yayin wannan lamari. Kaza lika a ranar Lahadin, sojoji sun harbe wasu mata 'yan kunar bakin wake su biyu dake dauke da ababen fashewa, yayin da suke kokarin tsallaka shingen tsaro da aka kafa a yankin Mammanti dake wajen birnin Maiduguri. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China