in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamandan Boko Haram ya mika wuya
2017-07-19 10:37:51 cri
Wani babban kwamandan Boko Haram tare da wasu 'ya'yan kungiyar 3 sun mika wuya ga dakarun tsaron Najeriya a jahar Borno dake arewa maso gabashin Najeriya.

Kakakin sojin Najeriya Birgediya Janar Sani Usman ne ya bayyana hakan a Abuja babban birnin kasar cewa, mayakan sun mika kansu ne ga runduna ta 120 ta sojojin Najeriya dake Goniri a jahar Borno.

Usman ya ce, a binciken da suka gudanar, sun tabbatar da cewa mayakan sun mika wuya ne sakamakon matsanancin halin da suka shiga, sannan sun gano cewa shugabannin kungiyar sun ba su gurguwar shawara.

Kakakin rundunar sojin ya ce mayakan sun yi danasanin jefa kansu cikin wannan muguwar dabi'a ta ta'addanci, kuma sun nuna gamsuwa da irin mu'amalar da sojojin Najeriya suka nuna musu a lokacin da suke hannun sojojin.

Sannan ya yi kira da sauran mayakan na Boko Haram da su amince su mika kansu domin kauracewa ayyukan ta'addanci da cutar da al'umma.

Usman ya ce akwai shiri na musamman da aka yi ga wadanda suka amince bisa radin kansu domin mika wuya, inda ya bayyana cewa ba za'a cutar da su ba.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China