in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 8 sun mutu sakamakon wani hadari a filin wasan kwallo a Senegal
2017-07-16 13:24:36 cri
A yayin wani wasan kwallon kafa zagayen karshe da aka yi a jiya Asabar a birnin Dakar na kasar Senegal, magoya-bayan kungiyoyin wasa biyu da suka fafata da juna, har wata katanga ta rufta a filin wasan, lamarin da ya yi ajalin mutane takwas.

Ministan kula da harkokin wasan motsa jiki na kasar Senegal, Matar Ba, ya tabbatar da cewa, cikin wadanda suka rasa rayukansu har da wata mata, kana an garzaya da mutane kimanin 60 asibiti don ba su kulawa.

Wadan da suka ganewa idonsu faruwar lamarin sun ce, yayin da ake shiga karin lokaci na wasan, magoya-bayan kungiyar wasan kwallon kafa ta Ouakam ta fara jefa duwatsu kan magoya bayan dayar kungiyar, lamarin da ya tilasta masu kallo suka fita daga filin wasan. Daga bisani 'yan sanda sun harba hayaki mai sa kwalla, a kokarin tarwatsa magoya-bayan kungiyoyin yan wasan biyu, lamarin da ya jefa mutane cikin fargaba.

Yayin da masu kallo ke kokarin ficewa daga filin wasan, wata katanga ta rufta ba zato ba tsammani. Wani mutumin da ya ganewa idonsa ya ce, katangar ta rufta ne a kan jama'a, 'babu tantama akwai mutane da dama da suka mutu.'(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China