Dakar zai karbi bakuncin wani dandalin kasa da kasa kan zaman lafiya da tsaro a Afirka
Babban birnin kasar Senegal, wato Dakar zai karbi bakuncin dandalin kasa da kasa kan zaman lafiya da tsaro a Afirka karo na uku daga ranar Litinin zuwa Talata, bisa taken "Afirka gaban kalubalolinta na tsaro: dubawa domin daukar nagartattun matakai". Dandalin zai tattara shugabannin kasashe, ministoci, shugabannin sojoji da jami'an diflomasiyya da suka fito daga yankuna daban daban, tare da buri guda na daukar wata hanyar zurfafa nazari kan matsalar tsaro a Afirka da kuma bullo da amsoshin da suka dace. (Maman Ada)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku