in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin sojojin Senegal zai shiga aikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake RDC-Congo ba da jimawa ba
2016-08-20 12:21:11 cri
Wani rukunin sojojin Senegal dake kunshe da manya da kananan hafsoshi 270, wanda ya hada kuma da mata jandarma guda goma sha biyar, zai isa nan bada jimawa a RDC-Congo domin karfafa aikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake jamhuriyar demokaradiyyar Congo (MONUSCO), in ji majiyoyin tsaro a ranar Jumma'a a birnan Dakar.

A yayin bikin mika tutar kasa ga rukunin, babban komandan jandarman, Jean Baptiste Tine, ya jaddada cewa bayan wani horon da ya basu damar kwarewa tare da tsarin aikin MDD da kuma yanayin ayyukan tabbatar da zaman lafiya, rukunin sojojin kasar Senegal na goma sha daya dake hanyar zuwa RDC-Congo ya shirya sosai wajen tafiyar da aikinsa yadda ya kamata.

Sojojin sun samu kwarewar da za ta ba su damar shiga ayyukan 'yan sandan MONUSCO. Muhimman ayyukansu za su hada da ba da kariya ga fararen hula, tabbatar da zaman lafiya da maido da ikon kasa, kawo gyaran fuska ga bangaren tsaro da kuma tallafawa ayyukan zabuka idan akwai bukata, in ji komandan Tine.

Hafsan ya kuma bukaci mambobin wannan rukuni da su girmama dokokin da ake bi wajen gudanar da ayyukan al'ummar Congo, musammun ma girmama al'ummomin kasar da kuma shugabannin kasar, tare da sanya kwarewarsu a sahun gaba. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China