Yau Alhamis ne rundunar tsaron kasar Kamaru ta tabbatar da cewa, wani harin kunar bakin wake da aka kai jiya da dare a wani yanki da ke kusa da iyakar kasar Najeriya, a arewa maso gabashin kasar, ya yi sanadiyar mutuwar mutane a kalla 16 yayin da wasu 30 kuma suka jikkata. Rundunar tana zargin 'yan kungiyar Boko Haram da kai wannan hari. (Tasallah Yuan)