Rahotanni daga kasar Kamarun na cewa, an kai harin kunar bakin wake har sau biyu a wani matsugunin fararen hula a garin Kolofata da ke yankin arewa mai nisa na kasar, inda mutane a kalla 4 suka rasa rayukansu, yayin da wasu fiye da 20 suka jikkata.
An ruwaito mahukuntan wurin da kuma 'yan sanda na cewa, 'yan tawayen Boko Haram ne suka kai harin. (Tasallah Yuan)