Harin kunar bakin wake ya hallaka mutane uku a arewacin Kamaru
2017-06-10 17:44:18
cri
Wata majiya daga rundunar sojin kasar Kamaru ta ce, an kai harin kunar bakin wake wani sansanin soja, dake yankin arewa mai nisa na kasar da safiyar yau Asabar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum uku tare da jikkatar wani.(Murtala Zhang)