in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe gasar tuka keke ta kasa da kasa karo na 14 a Kamaru
2017-03-20 12:16:27 cri
A Jiya Lahadi 19 ga wata ne aka rufe gasar tuka keke ta kasa da kasa karo na 14 a kasar Kamaru, inda kungiyar kasar Jamus ta lashe gasa ta mutum daya, da kuma gasa ta kungiyoyi, yayin da tawagar kasar Morocco, wadda ta lashe gasar da aka yi a shekarar da ta wuce, ta kasance a matsayi na biyu a bana, ta fuskar gasa ta mutum daya da gasa ta kungiyoyi.

An bude gasar tuka keke ta bana ne a ranar 11 ga watan Maris, kuma hanyar da aka yi gasar ta kai tsawon kilomita 956.7, inda ta ratsa manyan yankuna biyar na kasar Kamaru.

Shugaban kungiyar masu tuka keke ta Kamaru, wadda da ta shirya gasar, Ornoch Yossi, ya yaba da yadda aka gudanar da gasar, inda ya ce, a wannan karo, an gayyaci kwararrun kungiyoyi da dama, kuma yana fatan 'yan wasan keke na Kamaru za su yi koyi da su.

Kungiyoyi 11 da suka zo daga kasashe 10 ne suka halarci gasar ta wannan karon, cikin har da kungiyoyi guda biyu na kasar Kamaru.

Kuma kasashen da suka halarci gasar sun hada da, Kamaru, Ruwanda, Cote d'Ivoire, Morocco, Congo(Kinshasa), Belgium, Faransa, Jamus, Holland da kuma Slovakia. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China