Rahotanni na cewa, wani mutum da ake zargin dan kungiyar Boko Haram ne ya tayar da bam a wannan rana da karfe 5 da rabi na yamma agogon wurin, a wata kasuwa dake Kolofata kusa da iyakar yankin da kasar Nijeriya, wanda ya haddasa mutuwar fararen hula a kalla 5 tare da raunatar mutane da dama, ciki har da maharin. (Zainab)