in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya gabatar da shawara hudu kan hana yaduwar makaman kare dangi
2017-06-29 13:42:16 cri
Zaunennen wakilin kasar Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana cewa, yaduwar makaman kare dangi da yadda ake jigilarsu babban kalubalane ne ga yanayin tsaro da zaman lafiyar kasa da kasa, a saboda haka hakkin dukkan kasashen duniya ne su hana yaduwar irin wadannan makamai.

Liu ya yi wannan kiran yayin taron bainar jama'a da kwamitin sulhu na MDD ya kira kan hana yaduwar makaman kare dangi a tsakanin bangarori wadanda ba su karkashin mallakar gwamnatocin kasashen duniya.

Dangane da wannan batu, Liu Jieyi ya gabatar da shawarwari guda hudu kan yadda za a magance wannan matsala. Na farko, a aiwatar da ra'ayi daya da aka cimma, domin warware matsalar daga tushe. Sa'an nan, ya kamata a karfafa ayyukan kasa da kasa wajen hana yaduwar makaman kare dangi. Haka kuma, a zurfafa hadin gwiwar kasa da kasa domin kyautata ayyukan da abin ya shafa. A karshe a dauki matakan da suka wajaba, domin aiwatar da kudurin kwamitin sulhu na MDD mai lamba 1540 a dukkan fannoni.

Bugu da kari, ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da karfafa hadin gwiwar dake tsakaninta da sauran kasashen duniya domin ba da gudummawa kan yadda za a kyautata tsarin hana yaduwar makaman kare dangi, yin rigakafin yaduwar makamai da kuma kiyaye zaman lafiya a duniya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China