in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kalla mutane 58 ne suka rasu sakamakon gobarar da ta tashi a Burtaniya
2017-06-18 13:16:09 cri
Rundunar 'yan sandan birnin London na kasar Burtaniya ta tabbatar da cewa, a kalla mutane 58 wadanda ba a san inda suke ba a halin yanzu, aka tabbatar da rasuwarsu sakamakon gobarar da ta tashi a wani dogon bene dake yammacin birnin London na kasar Burtaniya da safiyar ranar 14 ga wata, ciki har da mutane 30 da aka riga aka tabbatar da rasuwarsu a baya.

Kuma a halin yanzu, ana ci gaba da gudanar da bincike a wurin da gobarar ta tashi, kuma adadin wadanda suka mutu na iya ci gaba da karuwa.

A jiya Asabar, masu zanga-zanga da dama sun taru a wurin dake kusa da fadar firaministan kasar dake kan titin Downing lamba ta 10, domin neman firaministar kasar Theresa May ta yi murabus, sabo da zargin da iyalan wadanda suka rasu suka yi wa gwamnatin kasar Burtaniyan cewar, ba ta yi rigakafi da kuma gudanar da ayyukan agaji yadda ya kamata ba.

Kuma wasu suna ganin cewa, hadarin gobarar da ta tashi a kasar, ya nuna matsalolin kasar Burtaniya kan gudanar da bincike kan yanayin tsaron kasa. Baki daya akwai irin wannan dogon bene kimanin dubu hudu a duk fadin kasar Burtaniya, kuma galibi an gina su ne daga shekarar 1950 zuwa shekarar 1970 na karnin da ya gabata.

A safiyar ranar 14 ga wata ne, gobara ta tashi a wani dogon bene mai suna Grenfell Tower, inda mutanen kasar suke zama a ciki. Firaministar kasar Theresa May ta ba da umurnin gudanar da bincike kan wannan hadari. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China