A jiya Laraba ne, rundunar 'yan sandan kasar Somaliya ta sanar da cewa, ya zuwa yanzu harin boma-boman da aka kai a babban birnin kasar, Mogadishu ya haddasa rasuwar mutane a kalla guda 14, haka kuma, bayan aukuwar harin, maharan sun yi garkuwa da mutane a kalla guda 20, domin shawo kan 'yan sandan. Amma, a halin yanzu, ba a tabbatar da halin da suke ciki ba.
Haka kuma, 'yan sandan sun bayyana cewa, maharan sun kashe wutar lantarki a dakin cin abincin da suka kai harin, kuma, 'yan sanda ba su yi nasarar kama su ba, saboda duhun dare. Amma, a halin yanzu, 'yan sandan sun killace yankin gaba daya.
Kungiyar Al Shabaab ta kasar Somaliya ta sanar da daukar alhakin kai wannan hari. (Maryam)