Bisa labarin da aka samu, an ce, maharin ya shiga dakin cin abincin ne da mota, wadda aka dasa boma-bomai a cikinta, inda fashewar boma-boman ta haddasa rasuwar mutanen.
Haka kuma, an ce, galibin mutanen da suka je dakin cin abincin, jami'an gwamnatin kasar ne da kuma wasu matasa.
Ya zuwa yanzu, babu wata kungiyar da ta sanar da daukar alhakin kaddamar da wannan hari. (Maryam)