Ma'aikatar tsaron kasar Amurka ta fidda wata sanarwa dake cewa, a safiyar jiya sojojin Amurka sun kai harin ta sama, kan sansanin jam'iyyar dake kudu maso yammacin birnin Mogadishu, hedkwatar kasar ta Somaliya, domin mayar da martani ga hare-haren da jam'iyyar ta kaiwa sansanin rundunar sojan Somaliya da sauransu.
To sai dai kuma sanarwar, ba ta tabo batun ainihin wurin da aka kaiwa harin ko sakamakon da aka samu ba. (Fatima)