in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An nada mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Liu Zhenmin a matsayin mataimakin babban sakataren MDD
2017-06-09 13:36:43 cri

Ranar 8 ga wata ne babban magatakardar MDD Antonio Guterres, ya sanar da nada mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin Liu Zhenmin, a matsayin sabon mataimakin sa mai kula da harkokin tattalin arziki da zamantakewar al'umma, inda zai maye gurbin Wu Hongbo, mai rike da mukamin a yanzu. Wa'adin aikin mista Wu Hongbo zai cika ne a ranar 31 ga watan Yulin bana.

Yanzu Liu Zhenmin, shi ne mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin mai kula da harkokin nahiyar Asiya, da dokoki, da yarjeniyoyi, da iyakokin kasa da na teku. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China