in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kai hari kan sansanin dakarun MDD dake wanzar da zaman lafiya a Mali
2017-05-04 09:29:36 cri
An kai hari kan wani sansanin tawagar wanzar da zaman lafiya da Majalisar Dinkin Duniya ta tura zuwa Mali wato MINUSMA, a birnin Tombouctou dake tsakiyar kasar, lamarin da ya yi ajalin wani sojan wanzar da zaman lafiya, tare da jikkata wasu sojojin 9.

A cikin wata sanarwar da ta bayar, tawagar MINUSMA ta yi Allah wadai da wannan hari, inda ta yi kira ga bangarori daban-daban da su gudanar da bincike don bankado madugun da ya jagoranci shirya makarkashiyar kai harin, ta kuma jaddada aniyarta ta ci gaba da tallafawa kasar Mali gami da al'ummarta wajen farfado da zaman lafiya da kwanciyar hankali.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China