in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar masu fafutuka ta INM ta sanar da daukar alhakin kai harin ta'addanci a Mali
2017-01-19 19:32:44 cri
Kungiyar masu tada kayar baya ta INM mai alaka da Al-Qaeda, ta fitar da wata sanarwa ta kafar internet a kasar Mauritania a ranar 18 ga jiya Laraba, inda ta sanar da daukar alhakin kaddamar da harin ta'addancin nan na sansanin soji dake arewacin kasar Mali.

Kungiyar wadda ke da sansani a wasu yankunan arewacin nahiyar Afirka, ta bayyana cewa, sunan wanda ya kai harin Abdullah Hady, ko da yake ba ta yi wani karin haske game da shi ba.

A jiya Labara ne dai da karfe 8 da minti 40 na safe, aka kaddamar da harin bom da aka dana jikin wata mota, a sansanin sojin dake yankin Gao na arewacin kasar Mali, wanda nan take ya haddasa mutuwar mutane a kalla 50, tare da raunata mutane da dama.

An dai kafa sansanin da aka kaiwa harin ne don cimma yarjejeniyar shimfida zaman lafiya a kasar Mali, kuma sojojin kasar Mali da dakarun dake goyon bayan gwamnatin kasar ne ke jibge sojojin su a sansanin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China