An haifi Maiga a birnin Gao dake arewacin kasar Mali a shekarar 1958, ya fara zama ministan tsaron kasar Mali tun daga watan Satumba na shekarar 2016, kana ya zama mataimakin shugaban Jam'iyyar kawancen kasar Mali dake kan karagar mulkin kasar.
Ana fuskantar barazanar tsaro a kasar Mali, tun daga ranar 9 ga watan Maris, likitoci da malaman makarantu sun shiga yajin aiki. Kuma Modibo Keita ya yi murabus a ranar 7 ga wannan wata.
Ya zuwa yanzu, gwamnatin kasar Mali ba ta bayyana dalilin da ya sa Modibo Keita ya yi murabus din ba, kana ba ta bayyana yaushe za a kafa sabuwar gwamnatin kasar ba. (Zainab)