in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mali ta sanar da sake shiga halin dokar-ta-baci
2017-03-31 11:01:31 cri
Shugaban kasar Mali Ibrahim Boubacar Keïta, ya shugabanci taron ministoci a jiya ranar 30 ga wata, inda aka tsaida kudurin sake shiga halin dokar-ta-baci na tsawon kwanaki 10.

Gwamnatin kasar Mali ta bayar da sanarwa a wannan rana cewa, an shiga halin dokar-ta-baci a wannan karo don tinkarar barazanar ta'addanci, ta sanar da shiga halin dokar-ta-baci tun daga ranar 31 ga wannan wata na shekarar 2017 a kasar Mali na tsawon kwanaki 10.

Sanarwar ta bayyana cewa, idan ba'a samu kyautatuwa ba, bayan da aka yi bincike kan halin tsaro na kasar Mali, gwamnatin kasar za ta tsawaita wa'adin halin dokar-ta-baci.

Sanarwar ta kara da cewa, za a amince da hukumomin da abin ya shafa da su magance ta'addanci da barazanar da ake yiwa tsaron jama'a da dukiyarsu yayin da aka shiga halin dokar-ta-baci.

A ranar 20 ga watan Yuli na shekarar 2016, kasar Mali ta sanar da kafa dokar-ta-baci har na tsawon kwanaki 10 tun daga ranar 21 ga wannan wata. Daga baya, an tsawaita wa'adin zuwa ranar 29 ga watan Maris na shekarar 2017. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China