in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yang Jiechi ya bayyana matsayin gwamnatin kasar Sin kan batun Siriya
2017-04-20 10:41:12 cri
Memban majalisar gudanarwa na kasar Sin, Mista Yang Jiechi, da babbar wakiliyar tarayyar Turai kan harkokin diflomasiyya da manufar tsaro, Madam Federica Mogherini, sun yi shawarwari bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da Turai karo na 7 jiya Laraba a birnin Beijing. Yayin da suke ganawa da 'yan jaridu bayan shawarwarin nasu, Yang Jiechi ya bayyana matsayin gwamnatin kasar Sin kan batun kasar Siriya.

Yang ya ce, kasar Sin ta ki yarda da duk wata aika-aikar yin amfani da makamai masu guba, kuma hanyar siyasa ce kadai ta fi dacewa wajen warware rikicin na Siriya. Kasar Sin na ganin cewa, ya kamata al'ummar Siriya su daidaita matsalar kasarsu, su ne za su yi zabi.

Sin da Turai sun cimma matsaya daya cewar, ya kamata a ci gaba da yin shawarwarin siyasa, da samar da tallafin jin-kai, da farfadowa gami da kare ababen more rayuwar al'umma a Siriyar, tare kuma da yaki da ayyukan ta'addanci, da kuma aiwatar da kudirorin kwamitin sulhun MDD yadda ya kamata.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China