in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya jaddada matsayin gwamnatin kasar Sin game da Siriya
2017-04-13 19:35:01 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi shawarwari tare da takwaransa na Falasdinu Riyad Al Malki yau Alhamis a nan birnin Beijing. Yayin da suke ganawa da manema labarai bayan shawarwarin, Wang Yi ya bayyana matsayin gwamnatin kasar ta Sin dangane da halin da ake ciki a Siriya.

Wang ya ce, halin da ake ciki a Siriya na kara tabarbarewa, lamarin da ya kasance abun damuwa matuka. Wang ya bayyana matsayin gwamnatin kasar Sin a fannoni uku, wato da farko Sin na adawa da duk wani yunkuri na amfani da makamai masu guba, ta kuma yi tofin Allah tsine game da aikata hakan. Kaza lika Sin na goyon-bayan gudanar da bincike sosai kan amfani da makamai masu guba da aka yi a Siriya, ta yadda za'a kai fa fitar da sakamako bisa gaskiya. Kana, duk wani matakin da za'a dauka, ya zama wajibi a dauke shi karkashin jagorancin MDD, tare da bin ka'idojin kasa da kasa.

Ya ce abu na biyu, kamata ya yi a mutunta cikakken 'yancin kan kasar Siriya, gami da ikon mallakar kasar. Kuma al'ummar Siriya ya dace su warware matsalar kasarsu bisa radin kansu.

Na uku kuma Sin na ganin cewa hanyar siyasa, ita ce kadai da za'a iya bi domin kaiwa ga warware matsalar kasar ta Siriya. Kuma kasar Sin ta na fatan bangarorin dake da ruwa da tsaki, musamman Amurka da Rasha, za su inganta mu'amala tsakaninsu, domin kaucewa zaman ja-in-ja tsakaninsu. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China