in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na adawa da dukkan kalamai da matakan dake dagula al'amura a zirin Koriya
2017-04-19 20:19:47 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana a nan birnin Beijing cewa, halin da ake ciki a zirin Koriya ya jawo hankali matuka. Kuma kasar Sin na adawa da dukkan wasu kalamai da matakan dake dagula yanayin da ake ciki a yankin.

Kwanakin baya ne mataimakin ministan harkokin wajen kasar Koriya ta Arewa Han Song-ryol, ya ce kasarsa za ta yi karin gwaje-gwajen makamai masu linzami a ko wane mako, da ko wane wata, kuma a ko wace shekara. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China