in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta sake yin kira ga Koriya ta Kudu da ta dakatar da shirin jibge na'urorin kakkabo makamai masu linzami na THAAD
2017-03-10 20:26:58 cri

Kasar Sin ta ce ba za ta tsoma baki a harkokin cikin wata kasa ba. Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang shi ne ya bayyana a yau lokacin da ya ambato batun tsige Park Geun-hye daga mukaminta na shugabar kasar Koriya ta Kudu a yayin taron manema labarai da aka shiryawa.

A matsayinta na makwabciyar Koriya ta Kudu, kasar Sin tana fatan samun kwanciyar hankali a harkokin siyasar Koriya ta Kudun.

Geng Shuang ya kuma sake yin kira ga Koriya ta Kudu da ta dakatar da shirin da ake na jibge na'urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin THAAD, a kokarin kawar da duk wani shinge na maido da kyakkyawan bunkasuwar huldar da ke tsakanin kasashen 2. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China