in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi Allah wadai da harin da aka kai a arewacin Syria
2017-04-16 13:26:42 cri
Jiya Asabar, babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya fidda wata sanarwa ta bakin kakakinsa, inda ya yi Allah wadai da harin da aka kai ga wadanda aka janye a birnin Aleppo na kasar Syria, ya kuma sa kaimi da a gurfanar da wadanda suka aikata wannan laifi a gaban kuliya.

Cikin sanarwar, MDD ta mika sakon ta'aziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, ta kuma yi fatan samun waraka cikin hanzari ga wadanda suka jikkata.

An gudanar da aikin kwashe mutanen ne bisa yarjejeniyar da aka kulla, shi ya sa, MDD ta yi kira ga bangarori daban daban da su tabbatar da tsaron mutanen da aka kwashe su daga yankin dake fama da hare-haren.

Haka zalika, wani jami'in gwamnatin kasar Syria ya bayyana a jiya cewa, an kai harin kunar bakin wake ga motoci da dama dake dauke da mabiya mazahabar Shia a yammacin birnin Aleppo na kasar, wadanda aka janye su daga yanki mai fama da hare-hare, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane a kalla guda 70, yayin da 128 suka jikkata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China