in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da jaridar musamman ta farko a Afrika kan taron dandalin tattaunawar koli ta hadin kan kasa da kasa game da shirin "Ziri daya da hanya daya"
2017-04-16 11:19:31 cri
kwanaki 30 gabanin bude taron dandalin tattaunawar koli ta hadin kan kasa da kasa game da shirin "Ziri daya hanya daya" ya shafa, jaridar El Pais wato muhimmiyar jaridar kasar Equatorial Guinea, da hadin gwiwar ofishin jakadancin kasar Sin da ke kasar, a jiya Juma'a sun kaddamar da wata jarida ta musamman game da dandalin tattaunawar.

karon farko ke nan da wata kafar watsa labarai ta kaddamar da jarida ta musamman game da dandalin tattaunawar .

Shugaban jaridar El Pais, ya ce ya yi farin ciki da jaridar ta kasance kafa ta farko wajen kaddamar da jarida ta musamman kan dandalin tattaunawar, ya na mai cewa wannan alama ce dake nuna cewa, bangarori daban-daban na kasar Equatorial Guinea, sun amince sosai da manufofin kasar Sin.

Jakadan Sin dake kasar Chen Guoyou, ya ba da sharhi tare da sa sunansa a jaridar ta musamman, inda ya ce kasar Sin na maraba da kasashen Afirka, ciki har da Guinea Ecuatorial da su shiga shirin "Ziri daya da hanya daya", don amfana da nasarorin da za a samu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China