in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Barkewar fada a Sudan ta Kudu ya yi sanadiyyar halaka mutane 16
2017-04-11 10:15:19 cri
Tawagar wanzar da zaman lafiya da Majalisar Dinkin Duniya ta tura zuwa kasar Sudan ta Kudu wato UNMISS ta bayar da wata sanarwa a jiya Litinin, inda ta ce, wata arangama ta barke a birnin Wau dake arewa maso yammacin kasar, lamarin da ya hallaka fararen-hula 16, tare da jikkata wasu 10.

Kasar Sudan ta Kudu na fama da tashe-tashen hankula a shekarun nan. A watan Afrilun shekara ta 2016, shugaban kasar wato Salva Kiir da madugun 'yan hamayyarsa wato Riek Machal, sun kafa gwamnatin hada kai ta rikon-kwarya, amma dakarun bangarorin biyu suka yi taho-mu-gama a watan Yulin bara, har Riek Machal ya tsere zuwa kasar waje. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China