in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta zargi rasuwar masu ceto 6 sakamakon farmakin da aka kai a Sudan ta Kudu
2017-03-27 09:53:45 cri
Mai daidaita harkokin jin kai na MDD dake kasar Sudan ta Kudu Eugene Owusu, a jiya Lahadi ya bayar da wata sanarwa, inda ya zargi masu kai hari kan jami'an kai agaji su 6 wadanda aka kashe har lahira wanda aka yi a ranar 25 ga wata a kan hanyarsu daga Juba, babban birnin kasar zuwa Pibor dake gabashin kasar.

Sanarwar ta ce, ba za a amince kan faruwar irin wannan lamarin ba a yayin da ake bukatar taimakon jin kai na gaggawa a kasar Sudan ta Kudu. Wannan ne kuma lamarin da aka fi samun rasuwar masu aikin ceto tun bayan afkuwar rikici a wannan kasa a watan Disamban shekarar 2013.

Game da hakan kuma, Owusu ya bayyana cewa, ba kawai wadannan lamuran kai farmaki sun kawo rasuwar masu aikin ceto ba ne, har ma sun kawo kalubale ga rayuwar 'yan kasar Sudan ta Kudu wadanda ke dogaro da samun taimako daga wajen masu aikin ceto na kasa da kasa.

Bisa kididdigar da sanarwar ta bayar, an nuna cewa, daga watan Disamban shekarar 2013 zuwa yanzu, a kalla masu aikin ceto 79 ne suka rasa rayukansu a sakamakon hare haren da aka kai musu. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China