in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a shawo kan tabarbarewar rikicin Siriya
2017-04-08 14:09:39 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin dake Majalisar Dinkin Duniya, Liu Jieyi ya bayyana a jiya Jumma'a cewa, gwamnatin kasar Sin na bada shawarar magance rikice-rikicen duniya ta hanyar hawa teburin sulhu, inda ya ce ya zama dole masu ruwa da tsaki su yi kokarin shawo kan ta'azzarar rikicin Siriya.

Liu Jieyi ya ce, daukar matakan soji ba zai kai ga warware rikicin ba, sai dai ma ya kara tsunduma jama'ar Siriya cikin mawuyacin hali, da kara ta'azzarar rikicin kasar gami da kara tashe-tashen hankula a wannan yanki, yana mai cewa, hakan ba zai dace da manyan bukatun al'ummar Siriya da ma sauran kasashen duniya ba.

Liu ya kara da cewa, ana samun bullar wasu sabbin al'amura yayin da ake kokarin yaki da ayyukan ta'addanci a wasu sassan Siriya, inda ya ce kamata ya yi kasashen duniya su yi hattara sosai, tare da murkushe dukkanin kungiyoyin 'yan ta'adda da MDD ta ayyana.

Da sanyin safiyar jiya Juma'a ne, jiragen yakin Amurka suka harba wasu makamai masu linzami guda 59, kan wani sansanin sojan saman gwamnatin Siriya na Shairat dake tsakiya maso yammacin kasar.

Karon farko ke nan da Amurka ta kaddamar da harin kan gwamnatin Siriya bayan darewar Donald Trump kan karagar mulkin kasar.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China