in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Syria ta goyi bayan kasa da kasa su yi bincike kan batun makamai masu guba
2017-04-07 10:36:02 cri
Mataimakin firaministan kasar Syria kuma ministan harkokin wajen kasar Walid Muallem, ya bayyana a ranar 6 ga wata cewa, kasar Syria tana nuna goyon baya ga kasa da kasa da su kafa kwamitin yin bincike kan batun yin amfani da makamai masu guba a jihar Idlib dake arewa maso yammacin kasar, amma ya kamata a magance yin amfani da kwamitin wajen cimma yunkurin siyasa. A wannan rana kuma, shugaban kasar Rasha Vlładimir Putin da firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu sun buga waya da bayyana cewa, game da batun yin amfani da makamai masu guba a kasar Syria, ba su amince da duk irin zargin da aka yi wa kasashensu kafin a yi bincike kan batun.

A ranar 4 ga wata a jihar Idlib dake kasar Syria, an kai harin makamai masu guba, wanda ya haddasa mutuwa da raunatar mutane da dama, kana ya jawo hankalin kasa da kasa sosai. (Zainab Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China