in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Iraki sun kashe jagora na biyu na IS
2017-04-02 13:30:29 cri
Rahotanni daga gidan talabijin na kasar Iraki na cewe, sojojin gwamnatin kasar sun kashe jagora na biyu na kungiyar IS, wato Ayad Hamid al-Jumaili, yayin wani luguden wuta da suka yi kwanan baya a yankunan yammacin kasar.

Rahoton ya ce, mutumin da aka kashe, ya zama jagora na biyu na IS, biyo bayan Abu Bakr al-Baghdadi.

Baya ga Jumaili din, akwai sauran wasu jagororin kungiyar IS wadanda aka kashe a yayin luguden wutan.

Tun a shekarar 2014 har zuwa yanzu, kungiyar IS sun kwace ikon yankunan arewa gami da na yammacin Iraki, tare da akasarin sassan kasar Siriya. A halin yanzu, sojojin gwamnatin Iraki na kokarin kwace ikon birnin Mosul daga hannun IS.

Tuni a ranar 31 ga watan Maris, hukumar leken asirin kasar Iraki ta ce, sojojin saman kasar sun yi luguden wuta kan maboyar dakarun kungiyar IS guda uku a garin Ba'aj dake kan iyakokin Iraki da Siriya, inda suka hallaka 'yan ta'adda 150 zuwa 200, wadanda suka shigo Iraki daga kasar Siriyar.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China