in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hare-hare a Iraki sun yi ajalin fararen-hula 543 a watan Maris
2017-04-02 13:29:06 cri
Tawagar samar da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya dake kasar Iraki ta fitar da wata sanarwa a jiya Asabar cewa, a watan Maris din bana, a kasar ta Iraki, fadace-fadace gami da hare-haren ta'addanci sun hallaka fararen-hula 543, tare da jikkata wasu 561.

Sanarwar ta ce, jihar Ninewa, inda birnin Mosul yake, ta zama jihar da ta fi samun rasuwa gami da jikkatar fararen-hula, inda mutane 367 ne suka rasa rayukansu, saura 174 kuma suka jikkata. Sai dai a jihar Bagadaza, inda fadar mulkin kasar wato birnin Bagadaza yake, akwai fararen hula 84 wadanda suka mutu, tare da jikkatar wasu 246.

A nasa bangaren, shugaban Tawagar samar da agaji ta Majalisar Dinkin Duniya dake kasar Iraki, Jan Kubis ya yi Allah da wadannan hare-haren da 'yan kungiyar masu tsattsauran ra'ayi suka kai kan farare-hula da gangan, kana ya yabawa kokarin da gwamnatin kasar Iraki ke yi, na kare fararen-hula lokacin yakin Mosul.

A halin yanzu, sojojin gwamnatin Iraki na ci gaba da gwagwarmaya domin kwace ikon yammacin birnin Mosul, yayin da mayakan kungiyar ta IS ke tsohon garin dake cibiyar birnin Mosul.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China