in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 279,000 ne a Iraqi suka kauracewa gidajensu sakamakon hare haren sojoji a Mosul
2017-03-28 10:47:20 cri
Mataimakin mai magana da yawun MDD Farhan Haq, yace kimanin mutane 279,000 ne a Iraqi suka tsere daga gidajensu a sakamakon hare haren da sojoji ke cigaba da kaddamarwa a Mosul, birnin dake arewacin kasar Iraqin.

Haq yace, daga cikin adadin, sama da mutane 220,000 ne suka fice daga gidajensu a yammacin birnin na Mosul wadanda suke makwabtaka inda sojojin ke yin lugudan wuta daga bangaren yammaci tun a karshen watan Fabrairu. Ana cigaba da kai tallafi ga wadanda rikicin ya daidaita har ma da mutanen da aka kwace iko da yankunasu matukar dai damar hakan ta samu.

Bugu da kari, jami'an kula da marasa lafiya daga yammacin Mosul sun sake karuwa a yankin har ma sun kafa wasu sabbin asibitoci biyu a yankunan Adhba da Hamam al Alil, dake kudancin birnin Mosul.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China