in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Masar da Falesdinu sun jaddada muhimmancin daftarin "kasashe biyu"
2017-03-21 13:21:41 cri
Bisa labarin da aka samu a jiya Litinin, an ce, shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi, ya gana da shugaban al'ummar Falesdinu Mahmoud Abbas, a birnin Alkahira fadar mulkin kasar, inda shugabannin biyu suka jaddada muhimmancin daftarin "kasashe biyu", wanda aka kulla a tsakanin Isra'ila da Falesdinu, suna masu bayyana shi a matsayin mataki da zai ba da tabbaci, wajen cimma burin shimfida zaman lafiya da lumana a yankin Gabas ta tsakiya.

Bugu da kari, an ce, shugabannin biyu sun yi kira ga kasashen Larabawa, da su yi hadin gwiwa domin kare ikon al'ummomin Falesdinu bisa doka, da kuma ba da taimako wajen gina kasar Falesdinu mai 'yancin kai, bisa yankin iyaka da aka shata a shekarar 1967. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China