in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burtaniya za ta fara aiwatar da shirin ficewarta daga EU a ranar 29 ga wata
2017-03-21 10:48:01 cri
Kakakin gwamnatin kasar Burtaniya ya bayyana a jiya Litinin cewa, firaministar kasa Theresa May, za ta sanar da fara aiwatar da yarjejeniyar Lisbon lamba ta 50, watau za a fara aiwatar da shirin ficewar kasar Burtaniya daga kungiyar tarayyar Turai EU a hukumance a ranar 29 ga wata.

Bugu da kari, ya ce, Theresa May ta aika wasiku ga sauran mambobin kungiyar EU 27, inda ta sanar da su cewa, kasar Burtaniya ta tsai da kudurin fara aiwatar da shirin ficewar kasar daga kungiyar EU, kuma Burtaniya tana sa ran yin shawarwari da EU kan batun cikin sauri.

A ranar 13 ga watan nan da muke ciki, majalisar dokoki Burtaniya ta zartas da daftarin ficewar kasa daga kungiyar EU, lamarin da ya sa, aka kawar da dukkan matsalolin dake gaban kasar ta fuskar dokoki wajen fara aiwatar da shirin ficewarta daga kungiyar EU.

Bugu da kari, sarauniyar Ingila Elizabeth II ta riga ta sa hannu kan daftarin, inda ta amince da firaministar kasar Theresa May da ta fara wannan aiki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China