in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
EU ta fidda shirye-shiryen da take fatan aiwatarwa karkashin mambobi 27
2017-03-02 11:10:35 cri
A jiya Laraba ne shugaban hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar kasashen Turai, watau EU Jean Claude Juncker ya gabatar da takardar makomar kungiyar bayan ficewar kasar Burtaniya daga cikin kungiyar a yayin cikakken zaman taron majalisar dokokin kasashen Turai da aka yi a birnin Brussels na kasar Belgium, inda ya gabatar da shirye-shirye guda biyar da kungiyar EU take fatan gudanar a shekarar 2025 karkashin mambobin kungiyar 27.

Gwamnatin kasar Burtaniya ta bayyana cewa, za ta fara aiwatar da shirin ficewa daga kungiyar EU kafin karshen watan nan da muke ciki, wannan ya sa aka mai da hankali matuka kan takardar da kungiyar EU ta fidda.

Kamar yadda ke kunshe cikin dokar kungiyar EU, Burtaniya za ta fara shirin ficewa daga kungiyar bayan da majalisar dokokin kasar ta kada kuri'ar yin hakan. Kasashe 27 ne za su rage a cikin kungiyar bayan kasar Burtaniya ta fita daga kungiyar a EU. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China