in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin Burtaniya ta kafa doka domin ficewar kasar daga EU
2017-03-14 11:18:43 cri

A jiya Litinin da dare ne, majalisar dokokin kasar Burtaniya ta zartas da dokar ficewa daga kungiyar tarayyar kasashen Turai wato EU, lamarin da ya kawar da matsala ta karshe ta fuskar doka ga gwamnatin kasar Burtaniya wajen fara shirin ficewar kasar daga kungiyar EU.

Wannan mataki na nufin, firaministar kasar za ta fara shiri da kuma yin shawarwari da kungiyar EU bayan ta sami izni daga sarauniyar kasar Burtaniya.

A wannan rana da dare ne, majalisar dokokin ta yiwa muhawara kan daftarin dokoki guda biyu da ta fitar game da ficewar kasar daga kungiyar EU. Kana kafin a kada kuri'u a majalisar dattijai kan wannan batun, an kuma kada kuri'u a majalisar wakilan kasar, inda aka tabka muhawara kan daftarin guda biyu, lamarin da ya nuna cewa, majalisar dattijai ta nuna hakuri da majalisar wakilan, inda aka kuma zartas da daftarin ficewar kasar Burtaniya daga kungiyar EU.

A farkon watan nan da muke ciki ne, majalisar dattijai ta yi muhawara game da zartas da daftarin ficewar kasar daga kungiyar EU, sa'an nan, ta bukaci gwamnati da ta yiwa fannoni biyu na daftarin gyaran fuska wadanda suka hada da kare 'yancin al'ummar kungiyar EU dake zaune a kasar Burtaniya yadda ya kamata, da kuma tabbatar da 'yancin majalisar dokokin kasar na tsai da kuduri kan ko kasar Burtaniya za ta iya ficewa daga kungiyar EU ko a'a. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China