in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaiministar Burtaniya ta ki sake kada kuri'u kan 'yancin kan Scotland
2017-03-17 11:59:12 cri
Jiya Alhamis 16 ga wata, firaministar kasar Burtaniya Theresa May ta yi musu kan bukatar da babbar jami'ar gwamnatin Scotland Nicola Sturgeon ta fitar domin neman sake kada kuri'u kan 'yancin kai na Scotland.

A ranar 13 ga wata, Nicola Sturgeon ta bayyana wa kafofin watsa labarai cewa, tana fatan sake kada kuri'a kan neman 'yancin kai na Scotland a tsakanin watan Yuli na shekarar 2018 zuwa watan Maris na shekarar 2019.

Dangane da wannan batu, firaministar Burtaniya Theresa May ta bayyana a ran 16 ga wata cewa, idan za a kada kuri'a kan neman 'yancin kai na Scotland, lamarin zai haddasa matsala ga kasar yayin shawarwari game da ficewar kasar daga kungiyar tarayyar turai EU, kuma wannan ba abu ne mai adalci ga al'ummonin Scotland ba, saboda an bukace su da su tsai da irin wannan kuduri mai muhimmanci a lokacin da ba su san wane irin dangantaka da za a kulla da kungiyar EU ba, har ma, ba a tabbatar musu wace irin makoma za su samu ba bayan samun 'yancin kai na Scotland. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China